Misira Ta Bayyana Goyan Bayan Ta Akan Yakar Kungiyar Boko Haram
Kasar Misira ta bayyana cewa tana goyan bayan gwamnatin Najeriya wajen yakar kungiyar Boko Haram. Jakadan Misira dake Najeriya ne ya fidda takardar a jiya inda jami’in ma’aikatar harkokin kasashen waje, Ahmed Abou Zeid ya rattabawa hannu.
Takardar tace: “Jami’i mai hudda da jama’a na ma’aikatar harkokin kasashen waje Ahmed Abou Zeid yayi Allah wadai da hate haren da aka kai wadanda sukayi sanadiyyar kashe mutane sama da 40.
“Muna kara jadda goyan bayan mu ga gwamnatin Najeriya. Kuma muna kira ga duniya da a hada hannu domin a kawo karshen ta’addanci.”
A makon daya wuce ne sojin Najeriya suka kashe sama da yan Boko Haram 35 bayan da suka yi awanni suna musayar wuta.
The post Misira Ta Bayyana Goyan Bayan Ta Akan Yakar Kungiyar Boko Haram appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read on NAIJ.COM.
Misira Ta Bayyana Goyan Bayan Ta Akan Yakar Kungiyar Boko Haram
Reviewed by Olusola Bodunde
on
11:44
Rating:
No comments:
Thanks for reading, please share this post and leave a comment. Your comment is important to us