Sports Betting

Trending

random

Fadar shugaban kasa ta yaba ma majalisar Najeriya

 

– Fadar shugaban kasa ta yaba ma sanatoci akan amincewa da kasafin kudi na 2016

– Kasafin kudin kimanin watanni 3 ke nana ana tanatance shi

kasafin kudi na 2016

Shugaban kasa Buhari a gaban majalisa lokacin da ya gabatar da kasafin kudin

amincewa da kasafin kudi na 2016 da yan majalisa sukayi ya samu yabo daga fadar shugaban kasa.

KU KARANTA: 

Inda yake ganawa da yan jarida, Ita Enang, mai taimaka ma shugaban kasa akan sha’anin majalisar dattawa, ya yaba ba duka sanatocin akan kokarin da sukayi akan kasafin kudi na 2016.

Yace ” Nabi duka yadda abubuwan ke tafiya kuma naga yadda sanatocin suka nunakwarewa wajen ganin an amince da kasafin kudin, musaam shugabanin kwamiti daban daban da yan kwamitocin.

Sannan kuma ya yaba ma sanatocin akan suka amince da MTEF da FSP wanda dashi ne aka amince da kasafin kudin.

Idan za’a iya tunawa, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kai kasafin kudin a ranar 22 ga watan Disamba. Amma daga baya an samu rudani wanda hakan ya sanya aka yima kasafin kudin gyare gayare.

Daga baya ne bayan da aka duba sai aka fara zama kan kasafin kudin in kwamitoci suka duba nasu sannan a jiya aka amince da kasafin kudin na 2016.

The post Fadar shugaban kasa ta yaba ma majalisar Najeriya appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read on NAIJ.COM.


Fadar shugaban kasa ta yaba ma majalisar Najeriya Reviewed by Olusola Bodunde on 23:33 Rating: 5

No comments:

Thanks for reading, please share this post and leave a comment. Your comment is important to us

All Rights Reserved by Naija News Live © 2014 - 2015
Powered By Blogger, Designed by Sweetheme

Contact Form

Name

Email *

Message *

Powered by Blogger.