Sports Betting

Trending

random

Sojojin Najeriya sun fatattaki yan Boko Haram a Jere

– Sojojin Najeriya sun hallaka yan Boko Haram a Dipcheri, Jere da Cholgo

– Sojojin sun amshe motoci, makamai da abubuwa daga hannun su.

Boko Haram

Wani sansani yan Boko Haram da ake konawa

boko haram

Sojin Najeriya bayan da suka hallaka yan Boko Haram suna zagaye

Bayan nasarar da aka samu daga sojojin runduna ta Task Force ta 151, 21 Brigade, sojojin Task Force na 155, Brigade ta 21 sun hallaka yan Boko Haram a Dipcheri, Jere da kuma a Chogolo.

boko haram

Sojin Najeriya rike da tutar yan kingiyar Boko Haram

Jami’i mai hudda da jama’a na sojin kasa na Najeriya, Kanar Sani Kakasheka Usman ya bayyana cewa “Sojojin Najeriya na rundunar Task Force na 155, Brigade ta 21 sun gudanar da aiki inda kori yan Boko Haram da suka rage a garuwan Dipcheri, Jere, da kuma Cholgo.

Boko haram

Motar da yan kungiyar suka gudu suka bari

Sojojin sun share duka garuruwan daga tsagerun ba tare da wata matsala ba inda suka kama wasu wadanda ake zargi guda 2.

Yan ta’addan kuma sun gudu sun bar mota guda 1, keke da kuma bindiga harlba ruga guda 2. Wannan aiki da akayi yana cikin tsarin zaman lafiya dole domin a kauda yan ta’addan daga yankin.

Bindigogin yan kungiyar

Bindigogin yan kungiyar

Jama’a su cigaba da taimakon mu da bayanai domin dakila dukkan aiyuka  yan ta’addan. Mun gode maku da gudunmuwar ku.

kungiyar Boko Haram

Wanni wanda aka kama wanda ake zargin dan kungiyar Boko Haram ne

Idan za’a iya tunawa, a makon daya wuce kasar Kamaru ta kama wani kwamandan yan Boko Haram a kuduncin kasar.

Kungiyar Boko Haram a Arewa maso Gabasihin Najeriya

Wani wanda ake zargin dan Boko Haram ne

A wani labarin kuma, yar kunar bakin waken da aka kama wadda ta bayyana cewa ita yar Chibok ce na cigaba da samun kulawa ta musamman. Gwamnatin Najeriya tuni ta aika da tawaga domin tantance bayanai.

The post Sojojin Najeriya sun fatattaki yan Boko Haram a Jere appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read on NAIJ.COM.


Sojojin Najeriya sun fatattaki yan Boko Haram a Jere Reviewed by Olusola Bodunde on 00:28 Rating: 5

No comments:

Thanks for reading, please share this post and leave a comment. Your comment is important to us

All Rights Reserved by Naija News Live © 2014 - 2015
Powered By Blogger, Designed by Sweetheme

Contact Form

Name

Email *

Message *

Powered by Blogger.