Sojin Najeriya na cigaba da samun nasara akan Boko Haram
Sojojin Najeriya na cigaba da samun nasara akan kungiyar boko Haram a cikin shekaru 7 da akayi ana gabza yakin.
Gwamnan jihar Borno, Kashim Shattima tare da Hafsin sojin Kasa, Tukur Yusuf Buratai suka bude wata hanya muhimmiya wanda ta jima a karkashin ikon Boko Haram. Hukumar Sojin ta saki wani bayani inda ta bayyana cewa ” A yau 6 ga watan Juli, an kafa tarihi akan yaki da ta’addanci a Najeriya.
A jiyan ne aka bude daya daga cikin hanyoyi mafi muhimmanci a jihar Borno. Wannan hanya itace hanyar Maiduguri -Mafa – Dikwa – Gomboru Ngala – Kamaru da abunda yayi gaba.
Sun bayyana cewa an samu nasarar saboda kokarin sojojin Najeriya, sauran jami’an tsaro da kuma Civilian JTF da sauran mutanen garin Borno masu son zaman lafiya
The post Sojin Najeriya na cigaba da samun nasara akan Boko Haram appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Nigerian newspapers 24/7.
No comments:
Thanks for reading, please share this post and leave a comment. Your comment is important to us