Gwamnan Da Bai Amshi Albashin Tun Hawa Shi
Gwamnan Jihar Filato Simon Lalong ya bayyana cewa bai amshi albashin ko na wata 1 ba tun hawan shi mulki a ranar 29 ga watan Mayu.
Gwamna Simon Lalong ya bayyana hakan ne wata ganawa da yayi da yan jarida a ranar Lahadi 6 ga watan Satumba domin bikin cikar shi kwana 100.
A ganawar, gwamnan ya bayyana cewa matsalar rashin kudin da Jihar ke fama dashi, shi ne ya nada nade naden mukamai.
Duk wadanda na nada basu amshi albashi kona wata 1 ba. Nima ban amsa ba. Muna so mu fara bikyan ma’aikatan gwamnati ne. Inda yake magana akan rikicin dake faruwa a jihar, gwamnan ya bayyana cewa an kawo Yan Sanda Mopol guda 150 a karamar hukumar Barikin Ladi da Riyom.
Akan kokarin da yake yi ya dawo kudaden da aka magabacin shi ya dauka, Gwamnan ya bayyana cewa ya hannunta maganar zuwa wajen hukumar hana almundahana.
Tun da wa’adin sati 2 dana basu ya wuce, na hannunta abun zuwa hukumar hana almundahana. Idan suka manta zani sake tuna masu.
Gwamnan ya bayyana cewa sun samu biyan Alawus din wata 5 cikin wata 7 daya gada wajen magabacin shi. Ya bayyana cewa zau biyan sauran akan lokaci.
Note: There is a poll embedded within this post, please visit the site to participate in this post's poll.The post Gwamnan Da Bai Amshi Albashin Tun Hawa Shi appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read on NAIJ.COM.
No comments:
Thanks for reading, please share this post and leave a comment. Your comment is important to us