Waiwaye: Wasu fittatun labaru na ranar Talata
Ga bitar wasu muhimman labaru da muka kawo muku a ranar Talata 2 ga watan Agusta:
Kanu ya magantu daga gidan Yari
Shugaban kungiya masu faffutukar kafa kasar Biafra, Nnamdi Kanu, wanda ke tsare a hannun hukumar tsaro ta farin kaya DSS, ya yi magana dangane da rahotanni da ke cewa ya na shirin kulla wata yarjejeiya tsakaninsa da kungiyar tsageru ta MEND da kuma gwamnatin tarayya domin a sake shi.
KU KARANTA: An gargadi wani dan fim kan taba Buhari
Fada Mbaka ya aika da babban sako a Buhari
Wani fada na darikar Katolika Ejike Mbaka, ya aikawa Shugaba Muhammadu Buhari wani babban sako a hudubarsa ta baya-bayan nan.
Shugaba Buhari zai sallami Ministocinsa 4
Bayan da Shugaban ya dauki tsawon lokacin don nada Ministocinsa, sai ga shi an shafe tsawon lokacin bayan nadin, amma kuma a cewar wasu, ba su tabuka wani abin ku-zo-ku-gani ba. Don haka ake hasashen cewa wasu shugaban kasa na iya saukesu.
KU KARANTA: Jibrin ya kai karar Dogara hukumar EFCC
Labari da dumi-dumi: Buhari ya salami shugabannin hukumomin ilimi
Shugaba Buhari ya salami kimanin shugabanni 17 na hukumomin ilimi da ke karkashin ma’aikatar ilimi ta kasar.
Mikel Obi ya yi canjin suna a hukumance
Fitaccen dan wasan kwallon kafa John Mikel Obi ya sauya sunanasa a hukumance, jaridar Miror ta rawaito cewa dan wasan ya gaji da yadda ba a fadin sunan daidai, don haka ya sauya
The post Waiwaye: Wasu fittatun labaru na ranar Talata appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Nigerian newspapers 24/7.
No comments:
Thanks for reading, please share this post and leave a comment. Your comment is important to us